[ad_1]
Junaid Muhammad wani dan majalisa a jamhuriya ta biyu ya ce wasu daga cikin yan uwan shugaban kasa Muhammad Buhari na san ya dawo da tsohon shugaban hukumar DSS ,Lawal Musa Daura bakin aikinsa.
Daura wanda aka kora daga bakin aikinsa bayan da ya umarci jami’an hukumar da su rufe kofar shiga majalisar tarayya, ya fito ne daga garin Daura dake jihar Katsina inda nan ne mahaifar shugaban kasa Muhammad Buhari.
A wata tattaunawa da jaridar The Punch, Muhammad ya ce “Akwai yunkuri daga wasu dake da alaka da shugaban kasa da suka fito daga Daura wadanda dole suna da alaka da Lawal Daura, da suke so su tafi Birtaniya su nemi Buhari ya warware abin da ya yi a fakaice ya dawo da Lawal Daura kana yakori mai bawa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro wanda kamata ya yi ace Daura yana kasansa amma ko kadan baya girmama shi hasali ma ba magana suke ba.”
Muhammad ya kuma bayyana cewa Adam Oshimhole, shugaban jam’iyyar APC bai dace ba da matsayin da yake kai a yanzu.
[ad_2]