Buhari na fuskantar matsin lamba kan ya dawo da Lawal Daura

[ad_1]








Junaid Muhammad wani dan majalisa a jamhuriya ta biyu ya ce wasu daga cikin yan uwan shugaban kasa Muhammad Buhari na san ya dawo da tsohon shugaban hukumar DSS ,Lawal Musa Daura bakin aikinsa.

Daura wanda aka kora daga bakin aikinsa bayan da ya umarci jami’an hukumar da su rufe kofar shiga majalisar tarayya, ya fito ne daga garin Daura dake jihar Katsina inda nan ne mahaifar shugaban kasa Muhammad Buhari.

A wata tattaunawa da jaridar The Punch, Muhammad ya ce “Akwai yunkuri daga wasu dake da alaka da shugaban kasa da suka fito daga Daura wadanda dole suna da alaka da Lawal Daura, da suke so su tafi Birtaniya su nemi Buhari ya warware abin da ya yi a fakaice ya dawo da Lawal Daura kana yakori mai bawa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro wanda kamata ya yi ace Daura yana kasansa amma ko kadan baya girmama shi hasali ma ba magana suke ba.”

Muhammad ya kuma bayyana cewa Adam Oshimhole, shugaban jam’iyyar APC bai dace ba da matsayin da yake kai a yanzu.




[ad_2]

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...