Ƴan bindiga sun sako mutane 56 da suka yi garkuwa da su jihar Niger

Yan bindiga sun sako sauran manoma 56 da suka yi garkuwa da su daga kauyen Adunu dake kusa da kauyukan dake karamar hukumar Paikoro ta jihar Niger bayan sun shafe watanni 6 a hannunsu.

Mazauna garin sun ce an sace mutanen ne a ranar 14 ga watan Maris inda suka cigaba da zama a hannun yan bindigar bayan da iyalansu suka gaza biyan kudin fansa a kan lokaci.

Tun da farko yan bindigar sun saki wani fefan bidiyo inda suka yi barazanar kashe ragowar mutane da suke rike da su matukar ba a biya kudin fansa ba.

Jami’in tsare-tsare na kungiyar Justice, Development and Peace Commission, Rabaran Bahago Dauda Musa ya ce ba a jima da sako mutanen ba.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...