Bene Ya Rufta Da Mutane A Abuja

[ad_1]








A yammacin yau Juma’a ne wani bene mai hawa biyar ya rufta a yankin Jabi da ke babban birnin tarayya Abuja.

Rahotanni sun bayyana cewa a lokacin da benen ya rufa, ana kan aiki a cikin sa.

Kimanin mutane hudu aka garzaya da su asibiti yayin da jami’an hukumar bayarda agajin gaggawa ke ci gaba da aikin ceto wadanda abun ya ritsa da su.

Jami’an na yunkurin kwashe baraguzan ginin domin ceto mutanen da ginin ya danne.

Wasu rahotannin sun nuna cewa cikin wadanda lamarin ya rutsa da su har da mata.

Izuwa lokacin da aka wallafa wannan labari, ba a san adadin mutanen da wannan abu ya ritsa da su ba.

Haka zalika ba a san musabbin zubewar ginin ba.

Birnin Tarayya dai na fuskantar ruwan sama kusan kowacce rana, wanda ko a yayin da jami’an agajin ke yunkurin ceto mutanen, ruwan sama ake ta tafkawa.




[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...