Bazan koma jam’iyar APC ba a cewar Adeleke

Ademola Adeleke gwamnan jihar Osun ya yi watsi da batun dake cewa akwai yiyuwar ya fice daga jam’iyar PDP.

Gwamnan ya ayyana biyayyarsa ga jam’iyar PDP a lokacin wani taro na musamman da aka gudanar da shugabannin jam’iyar a ranar Alhamis da daddare.

Adeleke ya ce jita-jitar  sauya shekarsa labarai ne  na  karya.

“Mutanena, dattawan jam’iya da kuma shugabanni ina ayyanawa a gabanku yau cewa bazan koma jam’iyar APC ba ko kuma wata jam’iya,” ya ce.

” Ina nan a PDP kuyi watsi da labaran karya,”

Kalaman na gwamnan na zuwa ne dai-dai lokacin da wasu jiga-jigan yan siyasa ke ficewa daga jam’iyar ta PDP.

More from this stream

Recomended