
Sanatoci uku na jam’iyar PDP daga jihar Kebbi sun amince su fice daga jam’iyarsu ya zuwa APC.
Sun yanke hukuncin komawa jam’iyar APC ne bayan wata tattaunawa mai tsawo da suka yi da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu a fadar shugaban kasa a ranar Juma’a.
A cikin wadanda suka halarci taron ganawar akwai shugaban jam’iyar APC, Abdullahi Umar Ganduje, gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, gwamnan Sokoto, Ahmad Aliyu da kuma ministan kasafin kudi da tsare-tsare, Atiku Bagudu.
Yarjejeniyar da aka cimma da sanatocin a ranar Juma’a wani cigaba da guguwar sauya sheka dake kadawa a kasarnan musamman ya zuwa jam’iyar APC mai mulki.
Sanatocin da za su sun sauya shekar sun hada da Adamu Aliero, Yahaya Abdullahi da Garba Maidoki.