Bauchi: ‘Za a rataye masu yi wa ƙananan yara fyaɗe’

Gwamnatin jihar Bauchi ta kafa wata doka da ake kira BAP wadda ta tanadi hukuncin kisa ta hanyar rataya ga duk wanda aka samu da laifin yi wa yara kanana Fyade.

Haka ma dokar ta tanadi ɗaurin rai da rai ga wanda ya yi wa babbar mace fyade da kuma ɗaurin shekaru 20 ga wadanda suka yi wa mace daya taron dangi.

Wannan dai na zuwa ne yayin da hukumomin ‘yan sanda a jihar suka ce sun samu rahotannin aikata fyade har 21 a cikin wata ɗayan da ya wuce kawai.

Ko a baya-bayan nan ma ‘yan sanda a jihar sun sanar da kama wani mutum da suke zargi da yi wa wata yarinya ‘yar shekaru uku fyade.

DSP Muhammad Ahmad Wakili, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar ta Bauchi ya ce dokar tuni aka amince da ita a majalisa kuma za a wallafa ta.

A cewarsa, tsakanin watan Yuli da Agusta sun gabatar da mutum 22 da ake zargi da aikata fyade gaban ‘yan jarida.

Ya ce sun yi hakan saboda “muna son mutane su kyamaci wannan abin su gane cewa idan an yi wa mace fyaɗe mai da al’uma baya ne saboda har ta gama rayuwarta da wannan (ƙyamar da ake nuna mata).”

DSP Wakili ya ce laifin fyaɗe ba wai yarinyar da aka yi wa ya shafa ba, laifin ya shafi ƙasa ne.

“Duk wanda muka kama ya yi fyaɗe, ba za mu yi wata-wata ba, sai mun gurfanar da shi gaban kotu, kuma wannan (dokar) BAP ita za mu saka ma shi a gaban kotu.” in ji DSP Wakili.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...