
Manajan Barcelona, Ernesto Valverde, ya ce sun fara zawarcin dan wasan Faransa Antoine Griezmann, bayan dan kwallon ya ce zai bar Atletico Madrid a bana, in ji jaridar Express.
Za a ba kocin Manchester City Pep Guardiola damar ci gaba da jagorantar kungiyar har tsawon shekara biyar masu zuwa kuma zai rika samun fam miliyan 100 yayin da albashinsa zai karu daga fam miliyan 15 zuwa 20, in ji jaridar (Sun).
Dan wasan Leicester City Harry Maguine, mai shekara 26, shi ne dan wasan da Guardiola yake sa ran zai maye gurbin Vincent Kompany wanda ya bar City a bana, a cewar jaridar Mail.
Manchester United tana duba yiwuwar kiran Alexis Sanchez, mai shekara 30, daga hutu don ya buga mata wasannin tunkarar kaka mai zuwa, kamar yadda jardar Sun ta bayyana.
Dan wasan Faransa, Kylian Mbappe, mai shekara 20, ya ce zai iya barin Paris St-Germain a kakar bana, wanda hakan ya sa manyan kungiyoyi kamar Real Madrid da Barcelona da kuma Manchester City fara zawarcinsa, in ji jaridar Express.