Gwamnan jihar Kogi kuma mai neman jam’iyar APC ta tsayar da shi takarar shugaban kasa ya ce baya tsoron tsayawa takara da tsohon shugaban kasa, Gudluck Jonathan dama duk wani da yake takara a APC.
Takarar Jonathan a APC ta samu goyon bayan wasu gwamnoni biyu da kuma wasu masu ruwa da tsaki da dama na jam’iyar a cewar wasu majiyoyi dake kusa da shi.
Bello ya fadi haka ne Jim kadan bayan da ya sayi fom din takara a hedkwatar jam’iyar APC.
Ya bayyana cewa matasa, dattawa, mata da kuma masu bukata ta musamman da kuma shugabanni dukkansu suna goya takararsa baya.