
Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya nuna alamun shirin komawa jam’iyar adawa ta ADC inda ya ce jam’iyar ta nuna alamun za ta iya kwace mulki a hannun jam’iyar APC a zaɓen 2027.
Gwamnan ya bayyana haka ne jim kaɗan bayan da ya yi wata ganawar sirri da wakilan shugaban jam’iyar ADC na ƙasa a ƙarƙashin jagorancin tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal ranar Talata a Bauchi.
Bala Mohammed ya bayyana cewa shugaban jam’iyar APC na ƙasa, David Mark ya mika masa goron gayyata ya zuwa jam’iyyar inda ya bayyanata a matsayin inda ya kamata ace sun koma sai dai ya ce har yanzu suna cigaba da tuntuba da tattaunawa domin daukr
Ya bayyana cewa nan bada jimawa ba za su ɗauki matakin da ya dace inda ake sa ran za su sanar da komawa jam’iyar a ranar Alhamis.
A cewarsa jam’iyarsa ta PDP bata da shugabanci da kuma alkibla kuma duk ƙoƙarin da aka yi na samun dai-daito ya ci tura hakan ya sa magoya bayansa ke matsin lambar a sauya sheka ya zuwa wata jam’iyar.

