‘Badakalar da aka tafka a zabukan fitar da gwani a Najeriya’

Mahmud Jega manazarci ne mai sharhi kan al’amuran siyasa a Najeriya, ya kuma yi wa BBC Hausa duba kan yadda zabukan fitar da gwanin jam’iyyu suka kasance a kasar.

APC

Zabukan fitar da gwani na jam’iyyu da aka gudanar a daukacin fadin Najeriya sun nuna cewa babu wani ci gaba a yanayin gudanar da siyasa a kasar tun bayan zabukan shekarar 2015.

Wadannan zabukan fitar da gwanin da aka zabi ‘yan takarar da za su rike kanbun jam’iyyun a zaben shekara mai zuwa ya haifar da haniya da yamutsi a daukacin fadin kasar.

A wasu jihohi batun ba shi da banbanci da yaki.

Matsala ta farko da jam’iyyun suka samu ita ce, samun masu neman takara masu yawan gaske a jihohi da dama.

Ga misali a jihar Borno, mutane 25 ne suka biya naira miliyan 22 suka sayi fom din da zai ba su damar tsayawa takarar gwamna a jihar.

A jihohin Nasarawa da Imo da Kwara da kuma sauran jihohi kuwa, masu neman takarar na da yawan gaske.

Wannan ya sanya aka samu zabukan cikin gida cike da rudani da hayaniya, kuma ya zama lamari mai wahala ga jam’iyyun su tabbatar da bin dokar jam’iyya.

Wata matsalar ita ce yadda wasu masu neman takarar suka dauki zaben fitar da gwanin a matsayin babban zabe.

Ga misali, a yankunan da jam’iyyar APC ke da karfi, wasu ‘yan takarar na ganin samun tikitin jam’iyyar tamkar nasara ce ga babban zaben, don haka suke yin bakin kokarin samun tikitin.

Kwatankwacin lamarin da ke a jam’iyyar PDP a jihohin da take da karfi, musamman a Kudu maso Gabashi da kudu maso Kudanci da kuma wasu jihohin arewaci da suka kunshi Taraba da Gombe.

A jihar Gombe, an fafata matuka a neman takarar kujerar gwamnan jihar inda ‘yan daba da ke goyon bayan wani mai neman takara suka yi dirar mikiya a wurin zaben, suka kuma yi kaca-kaca da shi bayan sun lura cewa zaben ba ya yi wa dan takararsu yadda yake so.

Matsalolin da su ka dabaibaye zabukan

A wurare da dama, jami’an jam’iyyu sun mayar da ranaku da wuraren zaben da kuma sunayen wakilan jam’iyyun a zabukan tamkar wasan yara.

An tabbatar da faruwar wadannan a manyan jam’iyyun APC da PDP. Sai jami’an su sanar da ranar zabe, take kuma su sauya wurin bayan sun bayar da dalilai marasa gamsarwa.

A kan yi hakan ne domin rikita tunanin wasu masu neman takarar da ba su ake so ba, don amfanin masu neman takarar da suke kauna.

Wannan dambarwar game da ranakun zaben ta kai har karshen mako lokacin da Hukumar Zabe Mai Zaman kanta INEC ta sanya domin kammala zabukan fitar da gwani.

A wani batun kuma, jami’an jam’iyyun na sanya ranakun zaben amma ba za su sanar da masu neman takara wurin da za a gudanar da shi ba, ko kuma su sanar da wurin amma su sauya a kurarran lokaci.

Duk da haka, wasu mashahuran dabaru na manyan ‘yan ‘jam’iyya kamar gwamnoni wajen murde zaben shi ne na sauya sunayen wakilan ana tsakiyar gudanawar da zabe.

Har wa yau, wata mummunar hikima ita ce tattare wakilan a boye su a wani otal, wanda ba mai iya kai wa gare su don hana wasu masu neman takarar bayyana masu manufofinsu domin su zabe su.

Wani muhimmin lamari kuma shi ne yadda kudi ka taka muhimmiyar rawa a siyasar ta Najeriya.

Wakilan jam’iyyun na karbar kudi makudai ta kowace fuska daga masu neman takara.

Wannan ce ta sanya wasu masu neman takarar a jam’iyyar APC, suka bukaci a gudanar da zaben fitar da gwani na ‘kai-tsaye’, inda duk dan jam’iyya da ke da rijista zai kada kuri’a ya zabi mai neman takarar da yake so.

Sun yi amannar cewa wannan tsarin ya fi inganci wajen tabbatar da karbuwar mai neman takara, kana zai taka birki ga wakilai masu kwadayi.

Gaskiyar lamari shi ne, shi ma zaben fitar da gwanin na ‘yan jam’iyya na da tsada saboda dole ne mai neman takara ya samu wakilansa da za su wakilce shi a mazabu, kuma dole ya dauki nauyin magoya bayansa domin su je su yi zaben.

An kuma samu wata matsalar saboda rashin sahihiyar rijistar ‘yan jam’iyyar.

Kamar yadda ta tabbata a Zamfara, zaben na kai-tsaye, ya haifar da hayaniya saboda kowa na zuwa filin zaben kuma ya yi ikirarin kasancewar shi dan jam’iyya.

Oshiomhole ya kawo rudani

A jam’iyyar APC musamman, shugabanta Adams Oshiomhole ya yi wasu abubuwa da suka kawo rudani.

Bisa alamu, an yi wa sanatocin da ba su sauya sheka tare da shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki alkawarin samun tikitin jam’iyyar ba tare da hamayya ba, musamman saboda mafi yawancinsu suna da matsala da gwamnoninsu.

Sai dai kuma, shugaban jam’iyyar ta APC na kasa ya yi wannan alkwarin ne ba tare da sanin gwamnoni ko sauran shugabannin jam’iyyar ba.

Daga nan sai suka yi kokarin cika alkawarin ta hanyar nuna rashin cancantar abokan neman takarar wadannan sanatocin, ko da kuwa sun sayi fom kuma sun ketare tantancewar.

Manyan abubuwan almara cikin zabukan fitar da ‘yan takara na wannan shekarar sun faru a jihohi biyu, wato Legas da Zamfara.

A jihar Legas, madugun jami’iyyar Asiwaju Bola Tinibu ya samu nasarar kawar da Gwamna Akinwunmi Ambode sannan ya haramta masa damar sake tsayawa takara.

Tinibun da ya tsayar da Ambode shekaru hudun da suka shude, sun samu sabani sakamakon wasu dalilai.

An samu kwan-gaba-kwan-baya a zaben fitar da gwamnan na jihar Legas inda masu gudanar da zaben da farko suka yi watsi da sakamakon zaben da aka gudanar, gabanin Oshimole ya sanya su karba kana su amince da shi.

Wani abun mamaki ga ‘yan Najeriya shi ne yadda shi Amboden ya komo ya amince da sakamakon.

Duk da bata mutumin da ya kayar da shi a zaben wato Sanwo-Olu, inda Amboden ya ce an taba tsare shi Sanwo-Olu din a Amurka bayan ya lika dala ta jabu yayin wata liyafa, kana an taba yi wa Sanwo-Olu jinyar tabin hankali a asibiti.

Dambarwar Zamfara

Dambarwar jihar Zamfara kuwa ta ma fi ta jihar Legos.

A nan mashahuran ‘yan takara guda takwas ne suke zawarcin kujerar gwamnan jihar, ciki har da wanda Gwamnan jihar mai barin gado Abdul’aziz Yari Abubakar ya tsayar.

Sauran masu neman takarar sun yi wa Yarin taron dangi kana suka yake shi, a mutu ko a yi rai.

Sau da dama mutane sun yi fitar farin-dango filayen zabe, kawai sai su ji sanarwar dage zaben saboda an samu barkewa rikici a wasu tashoshin zaben, tsakanin bangarorin da suke hamayya da juna.

Tambayar da al’ummar Najeriya ke yi ita ce, muddin wannan shi ne yadda jam’iyyun suka gudanar da zabukan fitar da gwanayensu, me zai iya faruwa yayin zaben kasa na shekara mai kamawa?

Ba ma fatan ganin ‘yan siyasa na fitar da maitarsu a fili, ko suna haifar da rikici ko kuma su ce a mutu baki daya, ko su take doka ko karya ka’idar dimokradiyya -da ta kamata su kare- don biyan bukatar kai.

Muddin yadda zabukan fitar da gwanayen shi ne abun da zai faru a zaben kasa na shekara mai kamawa, hakika akwai gagarumin aiki a gabanmu.

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...