Babu ƙamshin gaskiya a batun fara dauƙar ma’aikatan Immigration

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ce hukumar lura da shige da fice ta Najeriya a yanzu haka bata fara ɗaukar ma’aikata ba inda ta shawarci ƴan Najeriya da suyi watsi da duk wa ni talla da ake haɗawa a soshiyal midiya

Hukumar dake lura da ayyukan hukumomin Civil Defence, Gidajen Gyaran Hali, Hukumar Kashe Gobara da kuma Hukumar Lura Da Shige da Fice ita ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da sakataren hukumar,Jafaru Ahmed ya fitar ranar Asabar.

Sanarwar ta ce an jawo hankalin hukumar kan tallan da ake yaɗawa a kafafen sadarwar zamani ne cewa ta fara ɗaukar aikin Immigration na shekarar 2024.

Hukumar ta ce wannan aikin wasu ɓata gari ne dake neman zambatar yan Najeriya.

“Sanarwar ɗaukar aikin jabu ce kuma bata fito daga hukumar ba,” a cewar sanarwar.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...