Babban sifetan ƴansandan Najeriya ya bayar da umarnin dakatar da zirga-zirgar ababen hawa ranar zabe

Mai rikon mukamin Babban sifetan ƴansandan Najeriya, Muhammad Adamu ya bayar da umarnin dakatar da zirga-zirgar ababen hawa daga karfe 6:00 na safiyar ranar Asabar ya zuwa karfe 06 na yammacin ranar.

Mai magana da yawun rundunar, DCP Frank Mba shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Mba ya bayyana cewa an dauki wannan mataki ne domin kare lafiyar mutane da dukiyoyinsu da kuma inganta tsaro a kasa ya yin zaben shugaban kasa da za a gudanar ranar Asabar.

Ya kara da cewa hakan zai taimakawa jami’an tsaro wajen saka ido akan zaɓen wajen hana bata gari kawo tasgaro a zaɓen.

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...