Babban Hafsan Mayakan Saman Nigeria Ya Bukaci ‘Yan Bindigan Dake Zamfara Su Miƙa Wuya

[ad_1]

Air Marshal Sadique Abubakar, babban hafsan dakaru sama na Nigeria ya gayawa ‘yan bindigan dake ta da karin baya a zamfara cewa “su zo su ba da kansu, su ajiye makamansu, su bar wannan ta’addanci na kashe mutane haka siddan . Duk da yake motoci na da wahala shiga dazukan… mu a sama bamu da wannan damuwar. Saboda haka su daina wannan su ba da bindigoginsu…In sun ki abun da zai biyo baya bai da kyau”.

Kalamun na babban hafsan sojojin saman Nigerian tamkar gargadine na na karshe ga ‘yan bindigan dake jihar Zamfara da dazukan dake kewaye da jihar.

Aika aikar ‘yan bindigan a jihohin Kaduna, Katsina da Zamfara, na daukar sabon salo a kusan kwane lokaci. Ibrahim Janyau, shugaban wata kungiyar samar da zaman lafiya a Zamfara ya ce al’amarin jihar ya kai lahaula wala kuwata. Ya ce kisan da ake yi a jihar Zamfara ba’a yinshi a Borno ko Yobe. A rana daya an kashe mutane 200 a kauyen ‘Yar Galadima.

Ibrahim Janyau ya ci gaba da cewa maganar gaskiya sojojin sama ne maganin ‘yan ta’addan saboda dazukan da jihar ke dasu. Yace matakin da aka yiwa lakabin “Diran Mikiya” da sojojin suka yi, ya kawo masu sauki gwargwado. Barayin sun bazu wasu wurare a jihar, amma ana samun nasarar kashesu. Ya kara da kiran gwamnati ta kara sojojin sama a jihar.

Amma wasu masana tsaro na ganin barin wutar da sojojin sama ke yi a jihar Zamfara ka iya sa gungun barayin su sulale zuwa cikin jihohin dake makwaftaka da Zamfara.

Sai dai Air Mashal Sadique Abubakar, ya ce farmakin da su keyi bai tsaya a Zamfara ba kawai. Jiragen yakinsu na zuwa Katsina, Birnin Gwari har ma da dazukan dake cikin jihar Niger, saboda haka duk abun dake faruwa a kasa suna gani kuma suna daukan mataki

[ad_2]

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...