Farfesa na tattalin arzikin siyasa, Pat Utomi, ya bayyana cewa ba zai ƙara neman kujera ko karɓar wani mukami daga kowace gwamnati a Najeriya ba.
Utomi ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na tashar Channels Television a ranar Juma’a.
Ya ce burinsa kawai shi ne ganin an inganta rayuwar matasa da ƙarni na gaba, ba wai neman mukami ko kwangila daga gwamnati ba.
“Zan faɗi a sarari: ba zan tsaya takara ba, ba zan karɓi wani mukami ko kwangila daga kowace gwamnati a Najeriya ba. Abinda nake so kawai shi ne walwalar matasa da ƙarnin gobe,” in ji shi.
Utomi ya ƙara da cewa ya rayu cikin gaskiya ba tare da amfani da kuɗin gwamnati ko sata ba, yana mai jaddada cewa kalaman da wasu ke yi na cewa yana neman kwangila ba su da tushe.
Ba Zan Ƙara Karɓar Muƙamin Gwamnati a Najeriya Ba – Inji Wani Farfesa
