Gwamnatin Jihar Kano ta yi gargaɗi ga matasa masu tayar da tarzoma da tada hankali a cikin birnin, tana mai cewa ba za ta ƙara lamuntar rashin bin doka da oda ba.
Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Musamman, Air Vice Marshal Ibrahim Umar (rtd), ne ya bayyana haka a wata ziyara da ya kai yankunan da aka fi fuskantar rikice-rikicen ‘yan daba, ciki har da unguwar Kurna Tudun Fulani, inda wani matashi mai suna Abba Sa’idu ya rasa ransa sakamakon rikici tsakanin ƙungiyoyin ‘yan daba.
A cewarsa, gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ƙoƙarin samar da ayyukan yi ga matasa domin rage zaman banza da ya ke haddasa shiga harkokin ta’addanci da tada hankali.
“Tsaro ba aikin gwamnati kaɗai ba ne, kowa yana da rawar da zai taka. Dole ne mu haɗa hannu wajen tabbatar da zaman lafiya a Kano,” in ji Air Vice Marshal Ibrahim Umar.
A nasa jawabin, hakimin unguwar Kurna Tudun Fulani, Malam Usaini Ibrahim, ya bukaci gwamnatin jihar da ta kafa ofishin ‘yan sanda a yankin domin ƙarfafa tsaro, yana mai tabbatar da cewa al’ummar yankin za su ba da fili da ya dace don gina wannan ofishi.
A ƙarshe, gwamnati ta jaddada kudurinta na kare lafiyar jama’a da kuma shawo kan duk wata barazana ga zaman lafiya a fadin jihar.
‘Ba Za a Ƙara Yarda da Ƙeta Doka ba’: Gwamnatin Kano Ta Gargaɗi ‘Yan Daba
