Ba na tsoron fafatawa a zabe na gaskiya — Buhari

[ad_1]

Gwamnan jihar Lagos, wanda ake rade-radin cewa zai fice daga APC, na cikin tawagar Shugaba Buhari

Hakkin mallakar hoto
NIGERIA PRESIDENCY

Image caption

Gwamnan jihar Lagos, wanda ake rade-radin cewa zai fice daga APC, na cikin tawagar Shugaba Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ba ya tsoron fafatawa a zabe idan za a gudanar da shi cikin gaskiya.

Shugaba Buhari ya bayyana haka ne a yayin ganawa da ‘yan Najeriya mazauna kasar China a birnin Beijing inda yake ziyara.

A cewar sa, “Ba na jin tsoron karawa a zaben da za a gudanar cikin gaskiya saboda shi ne ya sa na zama shugaban kasa. Na san irin faman da na yi inda sau uku ina tsayawa takara ina faduwa zabe amma ina kalubalantar sakamakon sa a kotun koli.”

“Da na fadi a zabe karo na uku na ce ‘Allah ya saka min’; daga bisani aka yi amfani da fasahar na’ura wuririn gudanar da zabe kuma hakan ya taimaka mana,’ in ji Shugaba Buhari.

Shugaban na dai ya ayyana sha’awarsa ta sake tsayawa takarar shugabancin kasar a jam’iyyar APC mai mulki.

Ya ce zai sake tsayawa takarar ce domin ya kammala aikinsa na ci gaban kasa.

Sai dai ra’ayoyi sun sha bamban game da ayyukan da Shugaba Buhari ya ce ya yi.

Wasu ‘yan kasar na yabonsa bisa yaki da rashawa da cin hanci da matsalar taro, ko da yake wasu na ganin ya gaza fitar da kasar daga kangin tattalin arzikin da take ciki.

Kazalika babbar jam’iyyar hamayya da wasu ‘yan Najeriya na cewa Shugaba Buhari yana yaki da cin hanci ne kawai kan ‘yan adawa, inda yake kau da idanunsa kan ‘yan jam’iyyarsa ta APC da kuma wadanda suka kira shafaffu da mai.

Idan APC ta tsayar da shi takara, Shugaba Buhari zai fafata da watakila tsohon mataimakin shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar, shugaban majalisar dattawan kasar Bukola Saraki, tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Kwankwaso, gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal, ko dai duk mutumin da PDP ta tsayar takara a zaben 2019.

[ad_2]

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...