Kafofin yaɗa labaran Isra’ila sun ruwaito cewa an ga baƙin hayaƙi na tashi a wasu kamfanoni da ke yankin Negev a kudancin ƙasar.
Tashar Channel 12 da kuma jaridar Times ta Isra’ila sun wallafa hotunan hayaƙin, inda suka ce ya fito ne daga rukunin masana’antu na Ne’ot Hovav da ke birnin Beersheba.
Rahotanni sun nuna cewa babu wanda ya jikkata sakamakon lamarin.
Sai dai sojojin Isra’ila sun bayyana cewa gobarar ka iya tashi ne sakamakon ɓaraguzan makamai masu linzami da aka kakkaɓo, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito.
Lamarin na zuwa ne a daidai lokacin da rundunar sojin Isra’ila ta ce tana ƙoƙarin kakkaɓo makamai masu linzami da aka harba cikin ƙasar daga Iran.
Baƙin Hayaƙi Ya Tashi A Wani Yankin Masana’antu A Kudancin Isra’ila

