
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya gana da tsohon gwamnan Kano Rabi’u Musa Kwankwaso a gidansa dake Abuja
A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X Atiku ya ce sun samu damar tattauna batutuwa masu muhimmanci domin cigaban jam’iyarsu ta ADC.
“Mun yi tattaunawa mai muhimmanci kan cigaban jam’iyar mu ta ADC da kuma yadda zamu cigaba da aiki tukuru wajen ganin an samar da mulki mai inganci tare da fitar da jama’a daga mawuyacin halin da su ke ciki a ɗan ƙanƙanin lokaci,”.
Ana sa ɓangaren Kwankwaso ya wallafa wani sako a shafinsa na X inda ya ce ya ji daɗi da ziyarar da Atiku Abubakar ya kai masa.
Ya kuma yaba masa kan yadda su ka karɓe shi hannu bibbiyu a jam’iyar ADC inda ya yi alkawarin taimakawa jam’iyar ta samu nasara s zabuka masu zuwa a kowane mataki.

