Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin jihar Borno.

A ranar Talata ne ambaliyar ruwa ta raba miliyoyin mutane da gidajensu a unguwannin   Fori, Galtimari, Gwange, da kuma  Bulabulin dake Maiduguri.

Hukumar bada agajin gaggawa ta ƙasa, NEMA ta ce mutane 30 aka tabbatar sun mutu yayin da sama da mutane 400,000 suka rasa gidajensu sanadiyyar ambaliyar ruwan a birnin na Maiduguri.

Tuni gwamnatin jihar Borno ta buÉ—e sansanonin Æ´an gudun hijira domin tsugunar da mutanen da abun ya shafa.

Da yake magana a lokacin ziyarar a ranar Lahadi a Maiduguri tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana ambaliyar a matsayin wata babbar masifa.

” Duk da cewa mai gabatar da taro ya faÉ—i dalilin zuwan mu. Ina so ku sani cewa duk abun da ya shafi Borno to ya shafe ni,” a cewar Atiku.

Ya ce sun je garin ne shi da tawagarsa domin jajantawa Shehun Borno, gwamnatin jihar dama al’umma baki É—aya kan iftila’in da ya faru.

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...