Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin jihar Borno.
A ranar Talata ne ambaliyar ruwa ta raba miliyoyin mutane da gidajensu a unguwannin  Fori, Galtimari, Gwange, da kuma Bulabulin dake Maiduguri.
Hukumar bada agajin gaggawa ta ƙasa, NEMA ta ce mutane 30 aka tabbatar sun mutu yayin da sama da mutane 400,000 suka rasa gidajensu sanadiyyar ambaliyar ruwan a birnin na Maiduguri.
Tuni gwamnatin jihar Borno ta buÉ—e sansanonin Æ´an gudun hijira domin tsugunar da mutanen da abun ya shafa.
Da yake magana a lokacin ziyarar a ranar Lahadi a Maiduguri tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana ambaliyar a matsayin wata babbar masifa.
” Duk da cewa mai gabatar da taro ya faÉ—i dalilin zuwan mu. Ina so ku sani cewa duk abun da ya shafi Borno to ya shafe ni,” a cewar Atiku.
Ya ce sun je garin ne shi da tawagarsa domin jajantawa Shehun Borno, gwamnatin jihar dama al’umma baki É—aya kan iftila’in da ya faru.