[ad_1]
Hukumar zabe ta Najeriya INEC ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC mai mulkin kasar a matsayin wanda ya lashe zaben da ya gudana a jiya Asabar.
Farfesa Rotimi Ajayi na sashin nazarin kimiyyar siyasa na Jami’ar gwamnatin Tarayya ta Lokoja ne ya bayyana sakamakon.
Ya bayyana Haruna Isa na dan jam’iyyar APC, wanda ya sami kuri’u 26,860 a matsayin wanda ya lashe zaben:
“Haruna Isa ya cika dukkan sharuddan zabe, kuma hi ne ya sami kuri’u mafi yawa, saboda haka shi ne ya lashe zaben dan majalisar da ya gudana.”
An gudanar da zaben ne don maye gurbin dan majalisar wakilai na mazabar Lokoja/Kogi Koton-Karfe wanda wata babbar kotu ta sauke daga mukamin.
Dan takarar APCn ya fafata ne da wasu ‘yan takara su takwas daga jam’iyyu daban-daban.
Mai bi masa shi ne Abubakar B. Muhammad na jam’iyyar PDP wanda ya sami kuri’u 14,845.
Sai kuma Muhammad Kazeem na jam’iyyar ADC wanda shi kuma ya sami kuri’u 2,984.
PDP ta lashe zaben Kuros Riba
A jihar Kuros Riba ma an gudanar da zaben cike gurbi a mazabar gundumar Obudu.
Dan takarar jam’iyyar PDP Abbey Awara Ukpukpen ne lashe zaben da kuri’u 12, 712.
Ya doke sauran ‘yan takarar da suka fafata da shi, ciki har da na jam’iyyar APC wanda ya sami kuri’u 4,345.
An dai gudanar da zabuka guda hudu na maye gurbi a wasu mazabu dake ciki tarayyar Najeriya a jiya Asabar.
Mazabun sune na sanatoci a Arewacin Katsina da Kudancin Bauchi da na dan majalisar wakilai a mazabar Lokoja/Kogi Koton-Karfe na jihar Kogi, da kuma na dan majalisar jiha a Kuros Riba.
[ad_2]