![](https://arewa.ng/storage/apc-flag-1024x570-1-e16841499656699086390577347416790-600x334.jpeg)
Jam’iyar APC ta lashe dukkanin zaɓen shugabannin kananan hukumomin jihar Ekiti da kuma na kujerun kansiloli 177 da aka gudanar.
A ranar Asabar ne hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Ekiti ta gudanar da zaɓe a dukkanin ƙananan hukumomin jihar.
A cewar kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN jami’an tattara sakamakon zaben sune suka gabatar da sakamakon a hedikwatar hukumar dake Ado-Ekiti.
A ranar Lahadi ne shugaban hukumar, Cornelius Akintayo ya yabawa masu kada kuri’a kan yadda aka gudanar da zaɓen lafiya.