APC ta lashe zaɓen dukkanin shugabannin ƙananan hukumomin jihar Ekiti

Jam’iyar APC ta lashe dukkanin zaɓen shugabannin kananan hukumomin jihar Ekiti da kuma na kujerun kansiloli 177 da aka gudanar.

A ranar Asabar ne hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Ekiti ta gudanar da zaɓe a dukkanin ƙananan hukumomin jihar.

A cewar kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN jami’an tattara sakamakon zaben sune suka gabatar da sakamakon a hedikwatar hukumar dake Ado-Ekiti.

A ranar Lahadi ne shugaban hukumar, Cornelius Akintayo ya yabawa masu kada kuri’a kan yadda aka gudanar da zaɓen lafiya.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...