APC ta ce INEC ba ta iya dakatar da ‘yan takararta a Zamfara

Rikici ya hana zaben fitar da 'yan takara a Zamfara

Rikici ya hana zaben fitar da ‘yan takara a Zamfara

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta jaddada cewa ta aika da sunayen ‘yan takararta ga hukumar zabe ta INEC.

A cikin wata sanarwa da ta fitar da ke bayani kan matsalolin da ta samu a wasu jihohi, Jam’iyyarAPC ta ce tana da ‘yancin mika sunayen ‘yan takararta na Zamfara kuma hakkin hukumar zabe ne ta karba.

Ta ce INEC ba za ta iya hana wa ‘yan takararta shiga zabe ba a Zamfara.

Kuma ta ce ikirarin da hukumar zaben kasar ta yi game da sha’anin ‘yan takararta a Zamfara ba daidai ba ne kuma za ta ci gaba da bin matakan da suka dace domin tabbatar da ganin hukumar ta yi abin da ya dace.

A farkon watan Oktoba ne hukumar INEC ta ce jam’iyyar APC ba ta da hurumin tsayar da ‘yan takarar gwamna da na ‘yan majalisar jiha da na tarayya a zaben 2019, saboda ta kasa gudanar da zaben fitar da ‘yan takara.

Sai dai kuma jam’iyyar APC ta dage kan cewa tana da ‘yan takara kuma tuni ta mika sunayensu ga hukumar zaben.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...