Ana Cece-kuce a Jam’iyyar APC Kan Tsayawa Takarar Gwamna

Tuni dai ‘kanin Aisha Buhari matar shug aban kasa, ya dauki hoto tare da shugaban Muhammadu Buhari, rike da takardar tsayawarsa takara, batun da wasu ke fassarawa da goyon baya daga fadar shugaban kasa.

Wannan fitar guzan da ‘kanin matar shugaban kasar yayi, na neman rabuwa shugabanin jam’iyar APCn a jihar, da har wasu magoya bayan gwamnan jihar ke cewa ba zata sabu ba, wai bindiga a ruwa.

Hon. Hussaini Gambo Bello, na cikin hadiman gwamnan jihar Adamawan, wanda kuma ya bayyana irin damarar da suka yi don fuskantar wadanda ke neman kayarda gwamnan jihar Adamawa, Sanata Muhammadu Bindow Umar Jibrilla a cikin jam’iyar ta APC.

Tun farko da yake bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar gwamnan Adamawan ga shugabanin jam’iyar APC a jihar, Dakta Mahmood Halilu Ahmad, ya yi gugar zana ne da cewa sun shigo da kafar dama, domin kawo sauyi a jihar.

To sai dai kuma, yayin da ake wannan cece-kucen, shugabanin jam’iyar a jihar dake tare da bangaren gwamnan jihar sun musanta zargin cewa suna tare da wani bangare a wannan dambarwa. Ahmad Lawal shine sakataren tsare-tsare na jam’iyar APC a Adamawa. Ya ce duk wani zabe da za a gudanar a jihar Adamawa zasu tabbatar da cewa anyiwa kowa adalci.

Ya zuwa yanzu dai akwai kusan mutum hudu dake neman fafatawa da gwamnan jihar Adamawan Sanata Bindow Jibrilla, a inuwar jam’iyar APC, wadanda suka hada da tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa, EFCC, wato Mallam Nuhu Ribadu, wanda kuma lokaci ne ke tabbatar da yadda zata kaya.

Domin karin bayani saurari rahotan Ibrahim Abdul’aziz.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...