An yi zanga-zanga kan kwana 1000 da tsare el-Zakzaky

Daruruwan mabiya mazahabar Shi’a a Najeriya sun gudanar da zanga-zangar lumana a Abuja babban birnin kasar, domin juyayin cika kwanaki dubu daya da kama jagoransu Sheikh Ibrahim El-Zakzaky da kuma ci gaba da tsare shi tare da iyalansa.

Masu zanga-zangar sun rike kwalaye da hotunan malamin.

BBC ta tattauna da wasu daga cikin masu zanga-zangar, inda Abdullahi Muhammad Musa ya ce:

“Babban makasudun fitowarsu don gudanar da zanga-zangar shi ne domin a sako mana malaminmu, yau kwana 1000 cir yana tsare a hannun gwamnati ga ciwukan da aka ji mi shi, gashi kuma tare da matarsa ba a ba su cikakkiyar kulawa alhali kuma kotu ta ce a sake shi.”

Ya ci gaba da cewa, “So yanzu abin da muke so shi ne a sake shi tare da matarsa da kuma sauran ‘yan mazahabar da ke tsare.”

Abdullahi Muhammad ya ce “Tun bayan tsare jagoranmu, muna rayuwa ne cikin kunci, amma kuma duk da haka babu abin da aka fasa, don haka idan ma an yi mana haka ne don a hana mu wani abu a kasa, to babu abin da za mu fasa.”

Masu zanga-zangar sun yi tattaki a tituna a birnin Abuja musamman a kusa da sakatariyar gwamnatin Tarayya domin nuna rashin jin dadinsu.

An dai kama malamin ne a birnin Zariya a shekarar 2015.

Sai dai malamin ya yi shekara biyu yana tsare ba tare an gurfanar da shi a gaban kuliya ba, in ban da a ‘yan watannin baya da gwamnatin jihar Kaduna ta shigar da kara a gaban kotu.

Gwamnatin dai na tsare da Sheikh Zakzaky tun a shekarar 2015 bayan an samu wani tashin hankali tsakanin magoya bayansa da sojojin kasar a garin Zaria, lamarin da ya kai ga mutuwar daruruwan mabiya Shi’a.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...