An yi zanga-zanga a fadar shugaban ƙasa da majalisar ƙasa kan dawo da Sarki Sanusi

Wasu masu zanga-zanga sun yi jerin gwano ya zuwa ƙofar fadar shugaban ƙasa da kuma majalisar dokokin ta tarayya kan dawo da Sarki Muhammadu Sanusi kan karagar mulkin jihar Kano.

A ranar Alhamis ne gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da dawo da  Sanusi a matsayin Sarkin Kano bayan da ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautu ta jihar.

Majalisar dokokin jihar Kano ce tayi gyara kan dokar da tam ta raba masarautun jihar zuwa biyar ta kuma sauke Sanusi daga kujerarsa.

Duk da cewa wata kotu a jihar Kano ta bayar da umarnin cewa kada gwamnatin Kano ta aiwatar da kudirin dokar tuni gwamnatin ta yi gaban kanta ta naɗa Sanusi a matsayin Sarkin Kano na 16  a daular fulani.

Da yake magana da manema labarai a yayin zanga-zangar ranar Juma’a, Abdullahi Saleh jami’in tsare-tsare na ƙungiyar Northern Nigeria Peace and Development Foundation ya ce gwamna Yusuf ya ɗauki matakin ne domin batawa wanda ya gada wato tsohon gwamna Ganduje.

Saleh ya ce ya kamata shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya sanya baki domin gudun karyewar doka da oda.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...