An yi zanga-zanga a fadar shugaban ƙasa da majalisar ƙasa kan dawo da Sarki Sanusi

Wasu masu zanga-zanga sun yi jerin gwano ya zuwa ƙofar fadar shugaban ƙasa da kuma majalisar dokokin ta tarayya kan dawo da Sarki Muhammadu Sanusi kan karagar mulkin jihar Kano.

A ranar Alhamis ne gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da dawo da  Sanusi a matsayin Sarkin Kano bayan da ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautu ta jihar.

Majalisar dokokin jihar Kano ce tayi gyara kan dokar da tam ta raba masarautun jihar zuwa biyar ta kuma sauke Sanusi daga kujerarsa.

Duk da cewa wata kotu a jihar Kano ta bayar da umarnin cewa kada gwamnatin Kano ta aiwatar da kudirin dokar tuni gwamnatin ta yi gaban kanta ta naɗa Sanusi a matsayin Sarkin Kano na 16  a daular fulani.

Da yake magana da manema labarai a yayin zanga-zangar ranar Juma’a, Abdullahi Saleh jami’in tsare-tsare na ƙungiyar Northern Nigeria Peace and Development Foundation ya ce gwamna Yusuf ya ɗauki matakin ne domin batawa wanda ya gada wato tsohon gwamna Ganduje.

Saleh ya ce ya kamata shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya sanya baki domin gudun karyewar doka da oda.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...