Tun bayan da wata kafar labarai ta ce Majalisar Dinkin Duniya ta kammala shirin kirkiro wata kasa daga Najeriya da Kamaru ranar 10 ga watan Yuli aka shiga cece-kuce da kokarin tantance sahihinacin labarin.
Tuni dai kafafen yada labaran Najeriya su ka ruwaito wasu masu ruwa da tsaki, ciki har da tsohon shugaban hukumar shata kan iyakokin Najeriya daga 1999 zuwa 2006, wato zuwa lokacin da aka yi yarjajjeniya kan yankin da ake takaddama a kai, Alhaji Dahiru Bobbo, ya na karyata labarin da kafar mai suna WazobiaReporters ta yada.
(Taswirar Najeriya da Kamaru)
A cewar kafar labaran ta WazobiaReporter, kasar da za a kirkiro mai suna United Nations Organization (UNO) State of Cameroon a Turance, ko kasar Kamaru kirkirar UNO, za ta kai ga raba Najeriya da kananan hukumomi 24.
Kafar labaran ta ce Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya na lokacin Kofi Annan, ya gayyaci Shugaban Najeriya na lokacin, Olusegun Obasanjo da Shugaban Kamaru Paul Biya, inda su ka rattaba hannu a watan Maris na shekarar 2003 kan yarjajjeniyar sallamar da sassan kasashensu da su ke takaddama a kansu.
A wata rubutacciyar takardar bayani da ya raba ma ‘yan jarida jiya Jumma’a, Shugaban hukumar tantance taswira da kan iyakoki na Najeriya na lokacin, Alhaji Bobbo ya yi shakulatin bangaro da zancen, kamar yadda wasu kafafen yada labaran kasar su ka ce majiyoyi a Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ma sun shiritar da zancen, kamar dai yadda Kamar yadda wakilinmu a Fadar Shugaban Najeriya, Umar Faruk Musa ya kalato mana.
Wakilanmu da su ka kalato bayanai na baya bayan nan, za su cigaba da bin diddigin wannan shu’umin al’amari don sanar da masu saurarenmu halin da ake ciki, idan baya ta haihu.