Wata kungiyar jin Æ™ai mai suna Sawaba Humanitarian Initiative ta gudanar taron addu’a na musamman domin kawo Æ™arshen matsalar tsaro da tattalin arziki dake wahalar da Æ´an Najeriya.
An gudanar da taron addu’ar ne a Dutse babban birnin jihar Jigawa bayan da duk Æ™oÆ™arin da jami’an tsaro suka yi na hana taron ya ci tura.
Daruwan-ÆŠaruwan mutane da suka halarci taron addu’ar sun bayyana damuwarsu kan makomar Æ™asarnan dai-dai lokacin da yunwa, cututtuka da talauci ke cigaba da kashe mutane a kullum a yayin da waÉ—anda suke kan mulki a ke cigaba da nuna ko-in-kula kan halin da ake ciki.
Da yake magana bayan taron addu’ar, shugaban Æ™ungiyar Sawaba Humanitarian Initiative na Æ™asa, Kwamared Umar ÆŠanjani Hadejia ya ce halin da ake ciki na nema yafi Æ™arfin talaka.
“Sai da na kasa riÆ™e hawaye bayan da naga yadda yunwa take wahalar da tsofaffi da yara ar Æ™auyukan Jigawa,”
“Babu É—an siyasa mai hankali da zai yi bacci lafiya bayan ganin abun da na gani a Æ™auyuka da dama,” ya ce .
Ya ce za gudanar da irin wannan addu’ar a Æ™ananan hukumomin jihar.