An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke Abuja, biyo bayan rikicin da ya barke tsakanin sojoji da wasu ‘yan kasuwa a ranar Asabar.

Wani faifan bidiyo da manema labarai suka gani a ranar Asabar ya nuna dimbin fararen hular da suka yi galaba a kan wasu sojoji yayin wani artabu da suka yi a Banex.

Hedkwatar tsaro, da mai magana da yawun rundunar sojin Najeriya, Onyema Nwachukwu, ba a samu damar jin ta bakinsu ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

A halin da ake ciki, wani dan kasuwa da ya bayyana sunansa da Abdul, ya shaida wa ƴan jarida a ranar Asabar  cewa rikicin ya barke ne a kan sayar da wayar salula.


Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ya ce kwamishinan ‘yan sandan, Benett Igweh ya tura jami’an hukumar bayar da taimakon gaggawa

Adeh ta tabbatar da cewa “CP ta tura tawagar sirri zuwa wurin.”

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...