Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke Abuja, biyo bayan rikicin da ya barke tsakanin sojoji da wasu ‘yan kasuwa a ranar Asabar.
Wani faifan bidiyo da manema labarai suka gani a ranar Asabar ya nuna dimbin fararen hular da suka yi galaba a kan wasu sojoji yayin wani artabu da suka yi a Banex.
Hedkwatar tsaro, da mai magana da yawun rundunar sojin Najeriya, Onyema Nwachukwu, ba a samu damar jin ta bakinsu ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
A halin da ake ciki, wani dan kasuwa da ya bayyana sunansa da Abdul, ya shaida wa ƴan jarida a ranar Asabar cewa rikicin ya barke ne a kan sayar da wayar salula.
Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ya ce kwamishinan ‘yan sandan, Benett Igweh ya tura jami’an hukumar bayar da taimakon gaggawa
Adeh ta tabbatar da cewa “CP ta tura tawagar sirri zuwa wurin.”