Labarin da muke samu daga majiyoyin mu dai na nuni ne da cewa babban jami’in sojan Najeriyar nan wato Manjo Janar Idris Alkali da muka baku labarin bacewar sa a kwanan baya an tsinci gawar sa.
An tsinci gawar sojan ne a garin Jos ta jihar Filato a kusa da asibitin koyarwa na jami’ar tarayya dake jihar akan hanyar zuwa matsugunin jami’ar na din din din.
Jami’an tsaron Najeriya ne suka gano gawar ta sa tare da wasu masu sana’ar adaidaita sahu a cikin wani kududdufi dake a garin.
Haka zalika dai majiyar tamu tace ana kyautata zaton ‘yan kabilar Birom ne dake a jihar suka kashe shi duk da yake dai har yanzu ba samu wani bayani ba daga hukumar sojin kasar game da lamarin.