An Tsinci Gawar Manjo Janar Idris Alkali, Sojan Najeriya Da Ya Bace Kwanakin Baya

Labarin da muke samu daga majiyoyin mu dai na nuni ne da cewa babban jami’in sojan Najeriyar nan wato Manjo Janar Idris Alkali da muka baku labarin bacewar sa a kwanan baya an tsinci gawar sa.

An tsinci gawar sojan ne a garin Jos ta jihar Filato a kusa da asibitin koyarwa na jami’ar tarayya dake jihar akan hanyar zuwa matsugunin jami’ar na din din din.

Jami’an tsaron Najeriya ne suka gano gawar ta sa tare da wasu masu sana’ar adaidaita sahu a cikin wani kududdufi dake a garin.

Haka zalika dai majiyar tamu tace ana kyautata zaton ‘yan kabilar Birom ne dake a jihar suka kashe shi duk da yake dai har yanzu ba samu wani bayani ba daga hukumar sojin kasar game da lamarin.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...