Wata kotu a jihar Adamawa ta bayar da umarnin tsare wani mutum mai suna Abubakar Abdulsalam, bisa zargin aikata lalata da wani yaro mai shekara 12 da kuma wasu ’yan mata biyu masu shekaru 8 da 10.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a unguwar Yolde Pate da ke karamar hukumar Yola ta Kudu, a lokacin da ake zargin Abdulsalam da aikata laifukan a lokuta daban-daban cikin watan da ya gabata.
An gurfanar da Abdulsalam a gaban Kotun Majistare ta biyu da ke Yola, inda aka tuhume shi da laifuka guda biyu: lalata da dan adam da kuma aikata abin da ya saba da dabi’ar dan adam, bisa tanadin sashe na 263 da 211 na dokar hukunta manyan laifuka ta jihar Adamawa da aka sabunta a shekarar 2018.
Dan sanda mai gabatar da kara, Insfekta Ibrahim Aliyu, shi ne ya gabatar da bayanan tuhuma a gaban kotu a cikin rahoton farko (FIR).
Alkali mai shari’a ya bayar da umarnin tsare wanda ake zargi a gidan gyaran hali da ke Yola har zuwa wani lokaci da kotu za ta ci gaba da sauraron shari’ar.
An tsare wani mutum a Yola bisa zargin lalata da yaro da kuma wasu ’yan mata biyu
