A Jihar Bauchi, wata kotu ta ba da umarnin tsare wani fitaccen malamin addinin Musulunci na jihar, Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi a gidan yari.
Ƴan sandan jihar ce ta gurfanar da malamin a gaban kotu ranar Litinin, bayan ta gayyace shi game da wani ƙorafi da aka shigar gabanta.
Matakin na zuwa ne sama da wata ɗaya bayan Hukumar Shari’ar Musulunci ta jihar Bauchi ta ɗage wani zaman tattaunawa da ta shirya da Sheikh Idris Abdul’aziz, wanda aka yi zargin ya furta wasu miyagun kalamai a kan Annabi Muhammadu.
Sai dai malamin da wasu masu goyon bayansa sun musanta zargin, suna cewa kalaman Sheikh Idris Dutsen Tanshi, ba munana lafazi ba ne ga Fiyayyen Halitta.