An tilastawa dalibai mata kwana a cikin tsananin sanyi

[ad_1]

An sa yaran sun kwana a sanyi ne saboda ba su ci jarrabawa ba.

Hakkin mallakar hoto
NationBreakingNews

Image caption

An sa yaran sun kwana a sanyi ne saboda ba su ci jarrabawa ba.

An fusata iyayen dalibai a Kenya bayan tilastawa ‘yan mata sama da 30 kwana a tsakiyar wani fili cikin tsananin sanyi a wata makarantar kwana.

‘Yan matan da ke karatu a sakandaren Nasokol a garin Pokot da ke yammacin kasar, sun zargi shugabar makarantar da daukan wannan hukunci saboda rashin kokari a jarrabawa, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

A baya wani shirin bada tallafi a harkar tamaula ya taba jan hankali akan tsadar kudin makarantar, da kuma rashin samun biyan bukata la’akari da kokarin daliban, a cewar jaridar Daily Nation ta kasar.

Sai dai sabuwar shugabar makarantar ta yanzu ta bijiro da na ta tsarin da nufin inganta sakamakon jarabawar dalibai mata da kuma soke duk wasu tsare-tsare da ta gada daga magabanciyarta.

Yanzu kusan ‘yan mata da shekarunsu ke tsakanin goma sha biyar zuwa goma sha bakwai aka kora daga makaranta a yammacin ranar litinin saboda dalilai na rashin tabuka abin a zo a gani a jarabawa.

[ad_2]

More News

Ƴan sanda sun kama masu sayen kuri’a a zaben gwamnan Edo

Jami'an rundunar Æ´an sandan Najeriya sun kama wasu mutane 9 da ake zarginsu da sayen kuri'a da kuma mallakar kuri'ar da aka riga aka...

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...