An Samu Sabani Kan Umurnin Da ‘Yan awaren Biafra Suka Bayar

A jihar Imo, an samu rarrabuwar kawuna akan umurnin hana fita a ranar Juma’a, 14 ga wannan watan, wanda kungiyar ‘yan awaren Biafra ta IPOB ta ayyana a duk fadin yankin kudu maso gabas, don nuna fushi akan bacewar madugun kungiyar, Mista Nnamdi Kanu. da kuma iyayensa, wadanda har yanzu, ba’a gano inda suke ba.

Yayin da kungiyar ‘yan aware ta masu fafutukar Biafra ta ba da umurnin a zauna a gida a ranar Juma’a domin jawo hankalin hukumomi kan fitar da bayanai game da shugabansu Nnamdi Kanu, an samu rarrabuwar kawuna kan bin wannan umurni a jihar Imo, da ke kudu maso gabashin Najeriya.

Ni dan Najeriya ne kuma dan asalin kabilar Igbo. A game da ranar 14 ga watan nan da kungiyar IPOB ta hana fita, a gani na ba shi da wani tasiri, saboda zan bude shogona, in kuma gudanar da kasuwanci a ranar. Ba zan dauki ranar a matsayin ranar hana fita ba a kasar Igbo.” Inji Mista Ezealor Blessing Henry, mazaunin birnin Owerri.Ya ce amma idan ka dubi lamarin kungiyar IPOB da bacewar Nnamdi Kanu, gwamnatin tarayya ta san abin da ya fi dacewa ta yi game da

Ba zan dauki ranar a matsayin ranar hana fita ba a kasar Igbo.” Inji Mista Ezealor Blessing Henry, mazaunin birnin Owerri.Ya ce amma idan ka dubi lamarin kungiyar IPOB da bacewar Nnamdi Kanu, gwamnatin tarayya ta san abin da ya fi dacewa ta yi game da

Ya ce amma idan ka dubi lamarin kungiyar IPOB da bacewar Nnamdi Kanu, gwamnatin tarayya ta san abin da ya fi dacewa ta yi game da

‘yan gwagwarmayar nan da ke yunkurin ficewa. Mista Ezealor ya ce me yasa gwamnati ba za ta dauki matakan da za su kawo zaman lafiya mai dorewa ba? Ya kamata shugaban kasa ya dauki mataki, yana mai cewa kashe su ba shi ne abin yi ba wajen magance rikicin kungiyar IPOB. A cewar shi, “kamata ya yi shugaban kasa ya kirasu kan teburin sulhu su warware rikicin gaba daya.”A na ta ra’ayin kuma, Amuche Obialor, mai sayar da abinci

Mista Ezealor ya ce me yasa gwamnati ba za ta dauki matakan da za su kawo zaman lafiya mai dorewa ba? Ya kamata shugaban kasa ya dauki mataki, yana mai cewa kashe su ba shi ne abin yi ba wajen magance rikicin kungiyar IPOB. A cewar shi, “kamata ya yi shugaban kasa ya kirasu kan teburin sulhu su warware rikicin gaba daya.”A na ta ra’ayin kuma, Amuche Obialor, mai sayar da abinci

ta ce, “Ina so a sako Nnamdi Kanu daga duk inda yake. Yana da amfani a gare mu kuma muna bukatar kasar Biafra. Saboda haka, zan kasance a cikin daki a ranar. Ba zan fita ba.” Tun ranar Litinin, kwamishinan rundunar ‘yan sandan jihar, Malam Dasuki Galadanci ya yi gargadin cewa hukuma za ta cafke duk wanda aka tarar yana karya doka a game da umurnin hana fitan a ranar Juma’an, 14 ga wata. Ya yi wannan gargadin ne a taron hadin gwiwan da shugabannin hukumomin tsaro a jihar suka gudanar a Owerri, babban birnin jihar, inda ya kara da cewa, daga jiya Talata, hukumomin tsaro za su fara zagaye na nuna iko a sassan jihar, don isarwa ‘yan awaren IPOB sako.

Tun ranar Litinin, kwamishinan rundunar ‘yan sandan jihar, Malam Dasuki Galadanci ya yi gargadin cewa hukuma za ta cafke duk wanda aka tarar yana karya doka a game da umurnin hana fitan a ranar Juma’an, 14 ga wata. Ya yi wannan gargadin ne a taron hadin gwiwan da shugabannin hukumomin tsaro a jihar suka gudanar a Owerri, babban birnin jihar, inda ya kara da cewa, daga jiya Talata, hukumomin tsaro za su fara zagaye na nuna iko a sassan jihar, don isarwa ‘yan awaren IPOB sako.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...