An Samu Rudani Kan Ficewar Shekarau Daga PDP

[ad_1]

Tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim shekarau, ya ce bai fice daga jam’iyyar PDP ba kamar yadda rahotanni ke nunawa.

A yau Talata, mai ba Shekarau shawara kan harkokin yada labarai, Sule Ya’u Sule ya fito ya bayyana rashin gamsuwarsu da abin da ya kira “rashin adalci” da ake masu daga hedkwatar jam’iyyar da ke Abuja a hirar da ya yi da wakilin Muryar Amurka, Mahmud Ibrahim Kwari.

Rahotanni da dama sun ruwaito Sule yana mai bayyana cewa sun fice daga jam’iyyar bisa wannan dalili.

Amma shafin Twitter na tsohon gwamna Shekarau ya nuna cewa bai fita daga jam’iyyar ta PDP ba.

“Har yanzu ina @officialPDPNigeria, ana ci gaba da tuntubar juna, mai girma #IbrahimShekarau, Sarudaunan Kano na musanta ficewa daga jam’iyyar PDP.” Shafinsa na Twitter ya bayyana.

Reshen jam’iyyar ta PDP a kano ya fada cikin rudani, tun bayan da tsohon gwamna Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya fice daga APC ya koma jam’iyyar a watan Yuli.

Hakan ya haifar da takaddamar shugabancin jam’iyyar ta PDP tsakaninsa da Shekarau da Kwankwaso, lamarin da ya kai hedkwatar ta PDP daga Abuja ta rusa shugabannin jam’iyyar.

Bayan haka, an kafa kwamitin rikon kwarya mai dauke da mutum bakwai, matakin da bai yi wa bangaren Shekarau dadi ba.

Bangaren su Shekarau da Aminu Wali sun nuna korafi bayan da aka nada wani na hannun daman Kwankwaso a matsayin shugaban kwamitin rikon kwaryan.

Sannan mutum biyar cikin bakwai na mambobin kwamitin duk makusantan Kwankwaso ne, lamarin da ya sa bangaren su Shekaru suke zargin hedkwatar jam’iyyar da marawa Kwankwaso baya.

[ad_2]

More News

Ƴan sanda sun kama masu sayen kuri’a a zaben gwamnan Edo

Jami'an rundunar ƴan sandan Najeriya sun kama wasu mutane 9 da ake zarginsu da sayen kuri'a da kuma mallakar kuri'ar da aka riga aka...

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...