An samu fitowar masu zaɓe da yawa a garin Kankia a zaɓen cike gurbin da ake a Katsina

[ad_1]








An samu fitowar mutane masu yawa a zaben cike gurbin dan majalisar dattawa na mazabar arewacin Katsina da ake gudanarwa yau Asabar.

Fitattun yan takara biyu a zaben, Ahmad Babba Kaita na jam’iyar APC da kuma Alhaji Kabir Babba Kaita na jam’iyar PDP sun fito ne daga gida daya.

Wakilin jaridar Daily Trust ya lura cewa an samu fitowar jama’a masu yawa a tashoshin zabe daban-daban dake garin.

Da yake magana da manema labarai, tsohon dantakarar kujerar gwamnan jihar karkashin jam’iyar PDP a zaben shekarar 2015, Alhaji Musa Nashuni ya yabawa jami’an ƴansanda da kuma hukumar zabe kan yadda ake gudanar da zaben lami lafiya.

“Na ji dadi zaben yana gudana cikin lumana.tabbas wannan zaɓen cike gurbin zai bawa yan Najeriya kyakkyawan fata cewa za a gudanar da zaɓen shekarar 2019 lafiya,” ya ce.




[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...