[ad_1]
Kotu ta ba da belin dan jaridan kafar yada labarai ta Premium Times, Samuel Ogundipe, wanda jami’an ‘yan sanda suke tsare da shi tun ranar Talata.
Da safiyar ranar Juma’a ce aka saki, Mr Ogundipe bayan da alkalin kotun Abdulwahad Mohammed ya ba da belinsa a kan naira dubu dari biyar da gabatar da wani wanda zai tsaya masa wanda zai kasance mazaunin Abuja ne.
An sako dan jaridan ne bayan cika wadannan sharuddan na beli.
A ranar Laraba ne dan jaridar ya gurfana a gaban kotu ba tare da lauyansa ba.
A wannan ranar alkalin kotun ya amince da bukatar da rundunar ‘yan sanda ta shigar, inda ta nemi a ba ta damar ci gaba da tsare dan jaridar har zuwa ranar 20 ga watan Agusta.
Sai dai a zaman kotun na ranar Juma’a an bari lauyan dan jaridan ya shiga kotun, inda ya nemi kotun ta ba da belinsa.
Tun farko hukumar ‘yan sanda ta ce tana zargin Mista Ogudundipe ne da amfani da wasu bayannan sirri.
A cikin wata sanarwa da ke dauke da sa hannun kakakin hukumar ‘yan sanda, Jimoh Moshood, ta yi zargin cewa matakin da dan jaridan ya dauka, abu ne da ya saba wa dokokin tsaro kuma zai iya ta da husuma.
- An yi tir da tsare dan jaridar Premium Times a Najeriya
- Cogen NYSC: Me ya sa gwamnatin Buhari ta yi gum kan Kemi Adeosun
Sai dai lauyan kamfanin Premuim Times, Iti Ogunye, ya ce babu adalci a cikin sanarwar da hukumar ‘yan sanda ta fitar.
Tun a ranar Talata ne ake tsare da dan jaridan saboda ya ki bayyana majiyar da ta ba shi bayani kan wani labari da ya rubuta.
Labarin wanda wasu kafofin yada labarai suka rubuta ya bayyana cewa Baban Sufeton ‘yan sanda Ibrahim Idris ya mika wani rahoto ga Mukaddashin Shugaban Kasa Yemi Osinbajo.
Rahoton ya dora laifi ga shugaban hukumar tsaron farin kaya Lawal Daura, wanda da aka kora kan rawar da ya taka wajen tura jami’an tsaro zuwa majalisar dokokin kasar.
‘Yan Najeriya da kafofin watsa labarai na cikin gida da na waje da kuma kungiyoyin kare hakkin bil’Adama irin su Amnesty International sun yi Allah-wadai da matakin.
[ad_2]