An sake samun ƴan daba da suka tuba a Kano

Wasu sabbin ’yan daba 43 (Yan Daba) daga daga yankin Goburawa-Gangare da Tudun Fulani Quarters na karamar hukumar Ungogo ta Jihar Kano sun rungumi zaman lafiya tare da mika kansu ga rundunar ‘yan sandan jihar.

‘Yan barandan 43 sun sa adadin tubabbun ‘yan baranda a Jihar zuwa 143. ‘Yan barandan sun kasance tare da wasu dattijai, masu ruwa da tsaki a cikin al’umma.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, ya bayyana cewa wadannan ‘yan daba 43 na kungiyoyin biyu a baya sun yi artabu da juna (Fadan Yan Daba) sama da shekaru biyar.

Sanarwar ta ce, fadan ya kan kai ga kai hare-hare kan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, wanda ke haddasa asarar rayuka, da jikkatar mutane, da kuma asarar dukiyoyi.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...