
Gwamna Matawalle ya sha alwashin magance matsalar tsaro a Zamfara
Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta tabbatar da cewa an kashe mutum 34 a wani hari da ‘yan fashin daji suka kai kan kauyen Tungar Kahau cikin karamar hukumar Shinkafi.
Sai dai wasu mazaunan yankin Shinkafi sun ce mutanen da aka kashe sun kai 42, inda a ranar da aka kai harin aka samu gawawwakin mutum 40, kafin washe gari kuma a gano karin gawa biyu.
Wannan shi ne na baya-bayan nan cikin hare-haren ‘yan fashin daji wadanda suka addabi jihar Zamfara, da ma karin wasu jihohi da ke makwabtaka da ita.
Kwanan baya ma sai da aka kai hari kan kauyen Kanoma inda aka kashe mutane, lamarin da daga bisani ya janyo dakatar da wani babban basarake da kuma hakimin yankin.
Bayanai dai sun ce tuni mutanen Tungar Kahau suka tsere zuwa manyan garuruwa da ke ciki da wajen jihar Zamfara bayan harin ranar yammacin Juma’a.
“Gaskiyar magana, kauyen gaba daya ya watse, mutane duk inda ka duba kowa kuka kawai yake ta yi…kowa dar-dar yake yi kada dare ya yi masa a wannan kauye” in ji wani shaida.
Haka zalika wani da ya tsira daga harin ya shaida wa BBC cewa da yamma ne kwatsam maharan suka auka musu da harbin kan mai-uwa-da-wabi.
Ya ce da kyar Allah ya kubutar da shi tare da wani abokinsa, inda suka tsere zuwa garin Shinkafi, a cewarsa da dama ba su san inda dangin da ‘yan’uwansu suka shiga ba, bayan maharan sun kutsa kai cikin kauye.
Mai magana da yawun rundunar, Muhammed Shehu ya fada wa wakilinmu Sani Aliyu cewa tuni aka tura karin jami’an tsaro da suka je yankin don farautar maharan a cikin daji.