An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta jihar Filato.

Mai magana da yawun rundunar samar da tsaro a jihar Plateau ta Operation Safe Haven, Kaftin Oya James shi ne ya sanar da haka ga manema labarai.

Marigayin shi ne ke riƙe da sarautar Ciroman Kumbun dake gudumar Magun.

Shugaban kungiyar Gan Allah Fulani Development Association of Nigeria, (GAFDAN) Garba Abdullahi ya fadawa jaridar Daily Trust cewa marigayin ya ɓace bayan da ya bar asibiti domin ya sayowa matarsa da aka kwantar abinci.

“Bayan bincike na kwana huɗu an gano gawar a wata rijiya da ba a amfani da ita dake kusa da asibitin” a cewar Garba.

Shugaban ya shawarci mutanensu da su kwantar da hankali kuma kada su ɗauki doka a hannunsu.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...