An naɗa Damagum a matsayin sabon shugaban riko na jam’iyyar PDP

Kwamitin zartarwa na uwar jam’iyyar PDP ya sanar da naɗa Ilya Umar Damagum a matsayin sabon shugaban riko na jam’iyyar.

Kafin zama shugaban jam’iyyar Damagum ya kasance mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa shiyar arewa.

Debo Ologunagba mai magana da yawun jam’iyyar shi ne ya sanar da haka a Abuja.

Naɗin na Damagum na zuwa ne biyo bayan umarnin da wata kotu ta bayar da ya hana tsohon shugaban jam’iyyar Iyorchia Ayu daga ayyana kansa a matsayin shugaban ta.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...