An kuɓutar da wasu ɗaliban da aka sace a jami’a a Kogi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kogi ta bayyana cewa an ceto 14 daga cikin daliban jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence da ke Osara Okene da aka sace.

Idan ba a manta ba wasu ‘yan bindiga sun sace daliban ne da ke karatun jarabawar da za su yi ranar Alhamis da daddare.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigan sun shigo cikin wajen, inda suka shiga dakunan karatu uku, sannan suka fara harbin iska don tsorata daliban.

Sai dai da manema labarai sun tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, William Ayata ta wayar tarho inda ya ce, “Ya zuwa yanzu an ceto 14 daga cikinsu, mutanen mu suna cikin daji suna kokarin gano sauran.”

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...