An kuɓutar da wasu ɗaliban da aka sace a jami’a a Kogi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kogi ta bayyana cewa an ceto 14 daga cikin daliban jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence da ke Osara Okene da aka sace.

Idan ba a manta ba wasu ‘yan bindiga sun sace daliban ne da ke karatun jarabawar da za su yi ranar Alhamis da daddare.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigan sun shigo cikin wajen, inda suka shiga dakunan karatu uku, sannan suka fara harbin iska don tsorata daliban.

Sai dai da manema labarai sun tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, William Ayata ta wayar tarho inda ya ce, “Ya zuwa yanzu an ceto 14 daga cikinsu, mutanen mu suna cikin daji suna kokarin gano sauran.”

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...