[ad_1]
Akalla mutum 19 rahotanni suka ce an kashe a wani kazamin hari da ‘yan bindiga suka kai a kauyen Mailari da ke cikin jihar Borno yankin arewa maso gabashin Najeriya.
An kai harin ne a Mailari da ke yankin Guzamala, kuma ana kyautata zaton mayakan Boko Haram ne suka kai harin ranar lahadi da safe.
Rahotannin sun ce harin wanda aka kai ranar lahadi, ya tursasa wa daruruwan mutanen kayukan da ke yankin yin gudun hijira zuwa garin Munguno da suke makwabtaka.
Wani mazauni yankin da ya tsira daga harin ya shaida wa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa ya kirga gawawwakin mutane 19 da aka kashe cikinsu har da dan uwansa inda kuma ya ce an yi wa wasu da dama yankan rago.
Sai dai ya ce ba zai iya tantance ko ‘yan Boko Haram ne suka kai harin ba.
Baya ga kisan mutane kuma, rahotanni sun ce maharan sun bude wuta tare da kone gidaje da satar abincin mutane bayan sun shiga kauyen a ranar Asabar da dare.
Hare-haren da ake kai wa a baya-baya nan a yankin arewa maso gabashi, wani babban kalubale ne ga jami’an tsaron Najeriya da ke ikirarin karya lagon kungiyar Boko Haram.
[ad_2]