
Mutane biyu aka kashe tare da jikkata wasu biyar biyo bayan wani sabon rikici da ya barke a wurin zaben shugabannin mazabu na jam’iyar APC a Idanre dake jihar Ondo.
Rikicin ta faru ne a Ododo-Idanre hedkwatar ƙaramar hukumar Idanre ta jihar a lokacin da jam’iyar APC mai mulkin jihar ke gudanar da zaben shugabanni a mazabu 203 na ƙananan hukumomin jihar.
Rikicin na ranar Laraba ya samo asali ne daga rikicin da ya faru a sakatariyar jam’iyar APC dake Akure inda wasu da ake zargin bata gari ne suka farma taron masu ruwa da tsaki na jam’iyar inda su ka ci zarafin shugabannin jam’iyar.
Raphael Adetimehin kanin shugaban riko na jam’iyar na daga cikin waɗanda aka kaiwa hari a wurin taron.
Ya samu raunuka sanadiyar sararsa da adda bayan da maharan su ka yi zaton yayansa ne saboda yadda su ke kama sosai.
Shedun gani da ido sun bayyana cewa an kona motarsa a yayin da aka garzaya da shi ya zuwa babban asibitin Idanre inda yake can bai san halin da yake ciki.
Ade Adetimehin ya yi iƙirarin cewa harin na siyasa ne inda ya zargi Tajuddeen Adefisoye tsohon ɗan majalisar tarayya wanda kuma na hannun damar gwamnan jihar ne Lucky Aiyedatiwa da alhakin ɗaukar nauyin maharan.

