An kashe mutane 17 a farmakin yan bindiga kan yan ga hijira a Taraba

Akalla mutane 17 aka rawaito wasu da ake zargi mayakan kabilar Jukun ne su ka kashe bayan da suka kai wani tsararren farmaki kan wani s yan gudun hijira dake dawowa gidajensu a kauyen Tse Ajogo dake karamar hukumar Wukari ta jihar Taraba.

Akalla wasu mutane 10 ne suka jikkata a harin da aka kai  ranar 10 ga watan Disamba A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’ani tsaro

Ya ce maharan sun kai farmaki kan kauyen da misalin karfe 06:00 na asuba inda suka rika harbin kan me uwa da wabi kan mazauna kauyen dama yan  kuma gudun hijira inda ya kara a cewa wasu mutane da dama babu masaniyar inda suke a yayin da aka ƙona gidaje 7 a  harin.

Makama ya ruwaito wata majiya dake da masaniya kan harin na cewa wannan ne karo na biyu da ake kai farmaki makamancin haka a kan yan gudun hijirar dake komawa gidajensu.

Kauyen na da nisan akalla kilomita 3 daga garin Rafin Kada inda yake da sauki kai hari.

Kawo yanzu dai rundunar yan sandan jihar Taraba bata fitar da wata sanarwa ba kan harin.

More from this stream

Recomended