[ad_1]
Hukumar Aikin Hajji Ta Ƙasa, NAHCON, ta kammala aikin kwashe mahajjatan bana a daren ranar Juma’a.
Alhazan da suka hada da yan jirgin yawo da kuma jami’an hukumar ta NAHCON sun tashi daga filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja.
Da yake magana da manema labarai, kwamishina a hukumar dake lura da aiyuka, Abdullahi Modibbo ya ce hukumomin alhazai na jihohi sun yi rijistar maniyyata 40,000 ya yin da kusan maniyata 19,000 ne suka yi rijista ta kamfanonin shirya tafiye-tafiye.
Amma Modibbo ya ce jinkiri da aka samu wajen kammala jigilar alhazan ya faru ne sakamakon rashin kammala rijistar mahajjata da wuri ya karfafa cewa NAHCON ta yi kokari sosai wajen ganin an kammala aikin akan lokaci.
“Alhazai basu fito rijistar ba akan lokaci idan da sun fito a lokacin da ya dace to da za a kammala komai da wuri kafin yanzu,” ya ce.
Modibbo ya kara da cewa na sa ran fara kwaso alhazan ranar 27 ga watan Agusta.
[ad_2]