An kama wasu mutane da jabun sabbin kuɗin Naira

Jami’an yan sanda dake ofishin yan sanda na Igbo Eze a jihar Enugu sun samu nasarar kama wasu mutane biyu Joseph Chinenye mai shekaru 39 da kuma Onyeka Kenneth Ezeja an shekaru 29 da mallakar sabbin kuɗin Naira na jabu.

Mutanen biyu an same su da mallakar jabun kuɗi na yan naira 1000 har guda 180.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Enugu, Daniel Ndukwe ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce binciken da suka gudanar ya nuna cewa mutanen sun sayo kuɗin ne daga hannu wani mutum dake birnin Benin.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar ƙera bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...