An kama wasu mutane da jabun sabbin kuɗin Naira

Jami’an yan sanda dake ofishin yan sanda na Igbo Eze a jihar Enugu sun samu nasarar kama wasu mutane biyu Joseph Chinenye mai shekaru 39 da kuma Onyeka Kenneth Ezeja an shekaru 29 da mallakar sabbin kuɗin Naira na jabu.

Mutanen biyu an same su da mallakar jabun kuɗi na yan naira 1000 har guda 180.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Enugu, Daniel Ndukwe ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce binciken da suka gudanar ya nuna cewa mutanen sun sayo kuɗin ne daga hannu wani mutum dake birnin Benin.

More News

An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami'an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar...

Bala Muhammad ya zama shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP

An zaɓi gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Siminalayi Fabura zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers shi ne mataimakin shugaban...

Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan. A cewarsa, akwai bukatar...

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...