An kama waɗanda suka yi fyade wa yarinya a Adamawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta kama wasu mutane uku da ake zargi da aikata laifin fyade ga karamar yarinya.

Kakakin rundunar SP Suleiman Nguroje ne ya bayyana hakan a ranar Talata.

Wadanda ake zargin sun hada da Hassan Nasir mai shekaru 25, Uzairu Dan Fulani mai shekaru 25 da kuma Yahaya Edward, 26.

Suleiman ya ce an kama wadanda ake zargin ne da laifin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 15 fyade a karamar hukumar Mayo Belwa.

Ya kara da cewa biyu daga cikin wadanda ake zargin mazauna Sabon Pegi ne, Ngurore, Yola ta Kudu, dayan kuma dan unguwar Gabasa Mayo Belwa ne a karamar hukumar Yola ta Kudu.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...